Professional Documents
Culture Documents
NA
FITOWA TA DAYA
JULY, 2018
1
بسم الله الرحمن الرحيم
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai, tsira da
amincin Allah su tabbata ga annabi Muhammad manzon tsira
da mutanen gidansa da sahabbansa.
Hakika ilimin fiqhun musulunci yana daga cikin ilimomi masu
muhimmanci wadanda mutane suke bukatarsu saboda
lamuransu na yau da kullum, wannan yasa malamai suka
himmatu wajen dawwana wannan ilimin da kuma karantar
das hi.
A cikin wannan takardu mun tattaro muhimman FATAWOYI
wadanda suka shafi ‘yan’uwa mata daga cikin amsoshin
tambayoyinmu da muka rubuta a kafafen sada zumunta
(social Media), muna rokon Allah ya sanya albarka a cikinsu
ya zamar da su ambato mai kyau gare mu bayan
rayuwarmu.
2
1. SHIN MAI CIKI TANA IYA YIN HAILA ?
Tambaya:
Malam mai ciki za ta iya ganin Haila ?
Amsa:
Yawanci idan mace ta dau ciki jini yakan daina zuwa mata,
Imamu Ahmad yana cewa (Mata suna gane samuwar ciki da
yankewar jini) Idan mace mai ciki ta ga jini idan hakan ya
kasance kafin haihuwa da kwana biyu ko uku kuma a tare da
shi akwai ciwon haihuwa to wannan jinin haihuwa ne, idan
kuma kafin haka ne da lokaci mai tsawo, ko kuma tsakaninsa
da haihuwa ba yawa amma ba zafin haihuwa to wannan ba
biki ba ne, saidai shin haila ne ta yadda hukunce- hukuncen
haila za su hau kansa, ko kuma jinin cuta ne ta yadda
hukunce- hukuncen haila ba za su shafe shi ba? Anan
malamai sun yi sabani: Abin da yake daidai shi ne jinin haila
ne in dai ya zo a yadda ta saba yin jinin haila, saboda asali
duk jinin da ya zowa mace ana daukarsa a jinin haila, in dai
ba akwai wani sababi da zai hana shi ya zama haila ba,
kuma babu wani dalili a alqur’ani ko a sunna da zai hana shi
ya zama haila. Wannan shi ne mazahabar Maliku da Shafi'i,
kuma Baihaki ya hakaito hakan daga cikin maganganun
Ahmad.
Don haka yana tabbata ga mai ciki mai haila abin da yake
tabbata ga mai haila mara ciki sai a gurare guda biyu :
3
1. SAKI- Ya haramta a saki matar da idda ta wajaba a gare ta
idan tana haila, amma mai ciki ya halatta a sake ta a cikin
haila, saboda sakin matar da bata da ciki ya sabawa fadin
Allah ( Kuma ku sake su a farkon iddarsu) Suratud Dalak aya
ta 1, wato a farkon tsarkin da bai take ta a cikinsa ba. amma
sakin mace mai ciki tana haila sakin ta ne ga iddarta,
wannan ya hada da tana cikin haila ko tana cikin tsarki,
saboda iddarta tana kasancewa ne da haife wannan ciki, don
haka bai haramta a sake ta ba, bayan an yi jima’i da ita.
2. Mace mai ciki idan ta yi haila ba za ta yi idda da ita ba,
saboda iddar ta tana kasancewa ne da haife cikinta, wannan
ya hada da tana haila ko bata yi, saboda fadin Allah
madaukaki ( Iddar mata masu ciki tana kasancewa ne idan
su ka haife cikinsu). Suratud Dalak aya ta 4 Don neman karin
bayani duba : Dima'uddabi'iyya shafi na 11.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
4/2/2012
4
idan ya sake ta tana da ciki ko tana cikin tsarkin da bai take
ta ba, domin idan ya sake ta a cikin haila to ba ta fuskanci
idda ba, saboda hailar da ya sake ta a ciki ba za’a kirga da
ita ba, haka kuma idan ya sake ta tana da tsarki bayan ya
sadu da ita, domin bai sani ba shin ta dauki ciki ta yadda
iddarta za ta zama irin ta mai ciki ko kuma ba ta dauka ba ta
yadda za ta yi idda da haila, saboda rashin tabbacin haka sai
sakin ya haramta. Ya tabbata a cikin Bukhari da Muslim cewa
: Ibn umar ya saki matarsa tana haila, sai Umar ya bawa
Annabi s.a.w. labari, sai Annabi s.a.w. ya yi fushi, sai ya ce
"ka umarce shi ya mayar da ita sannan ya rike ta har ta yi
tsarki sannan ta yi haila, sannan ta yi tsarki, sannan in ya so
ya rike ta ko kuma ya sake ta kafin ya sadu da ita, wannan
ita ce iddar da Allah ya umarta a saki mata a ita" ana togace
gurare guda hudu wadanda sakin mace mai haila yake
hallata :
A. idan sakin ya kasance kafin ya kadaita da ita ko kafin ya
sadu da ita, to anan ya halatta ya sake ta tana haila, saboda
anan bata da idda, sakinta ba zai zama ya sabawa fadin
Allah madaukaki (Ku sake su a farkon iddarsu) ba.
B. idan ta yi hailar ne tana da ciki
C. idan ya sake ta ne bayan ta fanshi kanta, (KUL'I) to anan
babu laifi ya sake ta tana haila
D. Idan ya yiwa matarsa I'laa'i kuma aka yi watanni hudu bai
dawo ba.
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
21/2/2013
5
3. MANUFOFIN DA SUKA SA AKA HARAMTA ZINA!
Tambaya:
Assalamu alaikum malam Ina son karin bayani game da
manufofin sharia akan haramta zina.
Amsa:
Wa alaikum assalam Addinin musulunci ya zo don ya kare
tsatson Dan'adam da mutuncinsa, don haka ya shar'anta
aure kuma ya haramta zina, ga wasu daga cikin hikimomin
da haramta zina ya kunsa :
1. Katange mutane daga keta alfarmar shari'a.
2. Samar da Dan'adam ta hanya mai kyau, ta yadda za'a
samu wanda zai kula da shi, saboda duk wanda aka same shi
ta hanyar zina, to ba za'a samu wanda zai kula da shi ba
yadda ya kamata.
3. Saboda kada nasabar mutane ta cakudu da juna.
4. Katange mace daga cutarwa, ita da danginta, saboda zina
tana keta alfarmar mace, ta zamar da ita ba ta da daraja.
5. Kare mutane daga cututtuka, kamar yadda hakan yake a
bayyane.
6. Toshe hanyar faruwar manyan laifuka, miji zai iya kashe
matarsa, idan ya ga tana zina, kamar yadda mace za ta iya
kashe kwartuwar mijinta, daga nan sai a samu daukar fansa,
sai fitintinu, su yawaita.
7. Zina tana kawo gaba da kiyayya a tsakanin mutane.
8. Kare mutuncin yaron da za'a Haifa, domin duk yaron da
6
aka Haifa ta wannan hanyar zai rayu cikin kunci. Allah ne
mafi sani
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
21/4/2013
AHALUS-SUNNA BA ?
Tambaya:
Salam Malam ya halalta mace ta auri wanda ba dan Ahlul
sunnah ba? Don Allah ina son aba mu hujjoji saboda ta samu
abinda zata kare kan ta da shi.
Amsa:
To 'yar'uwa Annabi s.a.w. yana cewa : "Idan wanda kuka
yarda da addininsa da dabi'unsa ya zo muku, to ku aura
masa" kamar yadda Tirmizi ya rawaito a hadisi mai lamba
ta : 1084, Malamai suna cewa wannan hadisin yana nuni
akan cewa duk wanda ba'a yarda da addininsa ba, ba za'a
aurar masa ba, wannan sai ya nuna cewa duk wanda
bidi'arsa take kaiwa zuwa kafirci, bai halatta a aura masa 'ya
ba, don haka duk dan shi'an da yake zagin sahabbai ko yake
kafirta su bai halatta a aura masa 'ya ba, saboda ba musulmi
ba ne, domin ya karyata Allan da ya yarda da su, haka sufin
da yake allantar da shehunansa, ko yake ganin sun fi
annabawa, kuma yana sane yake hakan, ba jahili ba ne ko
kuma wanda yake da shubuhar da za'a iya warware masa .
Amma duk mai aikata bidi`ar da ba za ta kai zuwa ga kafirci
ba, to ya hallata a aura masa 'ya, kamar wanda yake yin
maulidi saboda son Annabi s.a,w.
7
Allah ne mafi sani ,
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
1-12-2014
Tambaya:
Dan Allah Malam Ina bukatar bayani akan "KUDRA da kuma
SUFRAH", Allah ya saka da Alkhairi.
Amsa:
To 'yar'uwa, wannan yana daga cikin mas'aloli masu
mutukar muhimanci, amma ga abin da ya sawwaka game da
hakan:
Sufra na nufin mace ta ga ruwa mai fatsi-fatsi kamar ruwan
ciwo, ya fito daga gabanta.
Kudra kuwa na nufin : ruwa ya ringa fitowa daga farjin
mace, wanda kalarsa ta ke kasancewa tsakanin fatsi-fatsi da
baki wato kamar ruwa gurbatacce,
Dangane da hukuncinsu kuwa : idan daya daga cikinsu ya
kasance a tsakiyar haila ne ko kuma yana hade da haila
kafin ta sami tsarki to wannan ana saka shi a cikin haila, idan
kuma bayan tsarki ne to ba haila ba ne saboda fadin Ummu
adiyya mun kasance ba ma kirga sufra da kudra bayan tsarki
a cikin haila) Abudawud ya rawaito shi da sanadi mai
inganci,
9
A hadisin A’isha kuma (Mata suna aiko mata da abin da suke
sawa lokacin da suke haila a jikinsa akwai sufra (wato ruwan
da yake kama da ruwan ciwo) sai ta ce musu kada ku yi
gaggawa har sai kun ga farin ruwa ya fito, ta yadda za mu yi
amfani da hadisin Ummu adiyya bayan an sami tsarki,
ma’ana ko ta ga sufra da kudra ba za ta kirga su a cikin haila
ba, hadisin A’isha kuma za mu yi amfani da shi idan tana
cikin haila ta yadda za ta kirga da su. Don neman karin
bayani duba: Dima'uddabi'iy a shafi na: 8
Allah ne mafi sani
6.12.2014
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
8. ADADIN SHAHIDAI DA INGANCIN SHAHADAR
WACCE TA MUTU A NAKUDAR CIKIN SHEGE?
Tambaya:
Assalamu alaikum Allah ya gafarta Mallam don Allah ina
Matsayar Malamai akan wadannan Mas'aloli, tare da
ambaton dalilai daga Qur,ani/Hadithi: Mutane nawa ne Ya
tabbata a Alqur,ani/Hadithi Sunyi Mutuwar Shahada? Domin
wani Dalibi abokina ya ce: Albani ya Ambaci : 9 a cikin
AHKAMIL JANA'IZ na duba ban gani ba, sannan idan Mace ta
mutu ayayin haihuwar Cikin Shege, shin itama ta yi
Shahada?
Amsa :
To dan'uwa shahidai suna da yawa: sun haura guda tara :
Ibnu- hajar yana cewa : "Mun tattara hadisan da suka yi
bayani akan shahidai sai muka samu sama da nau'i ashirin
na shahidai, Fathul-bary 6/43 hakanan Suyudi a littafinsa mai
10
suna : Abwabissa'adah fi asbabissa'adah, ya kawo sama da
guda talatin
Ka ga daga ciki, akwai wanda ya mutu a fagen daga, da
wanda ya mutu da ciwon ciki, sai wanda ya mutu a lokacin
kwalara sai kuma wanda ya mutu ta hanyar rusowar gini, sai
wanda ya nutse a ruwa, Hakanan wanda ya mutu wajan kare
dukiyarsa, da wanda kunama ko miciji ya harba, sai ya yi
ajalinsa, haka matar da ta mutu wajan haihuwa, dama
wanda namun daji suka cinye shi Haka wanda aka kashe shi
saboda kare iyalansa, duk wadannan sun tabbata a cikin
hadisai. Saidai wasu malaman suna ganin akwai sharuda
kafin mutum ya samu shahada:
Daga ciki kada ya zama: Ba ta hanyar gangaci ya mutu ba,
kamar mutumin da bai iya ruwa ba, ya shiga kogi, sai ya
mutu, sannan kar ya zama ta hanyar sabo ya isa zuwa
shahadar, kamar matar da ta mutu wajan nakudar cikin
shege, ko bawan da ya gujewa mai gidansa, sai ya mutu a
hanya.
wasu malaman suna ganinin hakan ba sharadi ba ne, tun da
hadisan ba su kayyade ba. Don neman Karin bayani duba:
Fataawal-kubra na Ibnu-taimiyya 3/22 da Mugni A l-muhtaj
3/166
Allah ne mafi sani
9-12-2014
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
Tambaya:
11
Salam malam don Allah ka taimaka min ka amsa tambaya
ta. ni dai malam gaskiya hankali na ya ki kwantawa
sakamakon al'adar wankan jego da ake yi a kasar hausa.
iyalina ta haihu an kawo wata tana yi mata wanka, to malam
ya hukuncin ya ke duba ga haramcin nuna tsaraici ga wani,
don Allah malam ka daure ka Amsa don hankalina ba'a
kwance yake ba.
Amsa:
To malam akwai hanyoyin na zamani wadanda za'a iya
amfani da su ba tare da an yi wankan jego ba, kamar amfani
da kwayoyi na asibiti, saidai idan ya zama babu makawa sai
an yi wankan na jego kuma wata ce za ta yi mata, kamar ya
zama haihuwar fari ce kuma babu halin da za'a iya sayen
kwayoyi saboda talauci, to hukuncin wannan zai yi daidai da
hukuncin likitan da take kula da lalurar mata, saboda shi ma
wankan jego ana yinsa ne saboda magani. A shari'ance ya
wajaba ga likita ya yi taka-tsantsan wajan kallon al'aurar
mara lafiya ta yadda ba zai kalli wani bangare na al'aurar
mara lafiya ba sai gwargwadon lalura, domin daga cikin
ka'idojin shari'a shi ne duk abin da ya halatta saboda lalura,
to ya wajaba a tsaya gwargwadon lalurar, wannan ya sa idan
da zai kalli sama da haka, sai ya zama mai laifi a wajan Allah.
Al'aurar mace ga 'yar'uwarta mace tana farawa ne daga
cibiya zuwa guiwa a zance mafi inganci, don haka mai
wankan jego za ta kalli gwargwadon abin da ya wajaba ta
kalla don tabbatar da lafiyar mai jego, idan kuma akwai
12
hanyar da za ta bi ta yi mata wankan ba tare da kallon
al'aurar ta ba, to wannan shi ne ya wajaba.
Duba kwatankwacin wannan mas'alar a Alkawa'idul kulliya na
Usman Shabirr shafi na : 222
Allah ne mafi sani
14-12-2014
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
13
11. ABUBUWAN DA AKE SO MIJI YA FI MATARSA DA SU
14
Malam menene hukuncin 'yan matan da suke bada
hotunansu ga tsofafi don su nema musu mijin aure?
AMSA:
Addinin musulunci ya haramta kallo zuwa ga matar da ba
muharrama ba, sai in akwai lalura, amma ya halatta ka kalli
mace, idan kana so ka aure ta, kamar yadda ya zo a cikin
hadisi, inda Annabi s.a.w. yake cewa: "Idan dayanku yana
neman aure, to in ya sami damar kallon abin da zai kira shi
zuwa aurenta,to ya aikata hakan" ABU DAWUD Malamai sun
yi sabani akan wurin da ya kamata mutum ya kalla a jikin
mace lokacin da ya je neman aure
1. Akwai wadanda suka ce zai kalli fuska da tafin hannu ne
kawai.
2. Wasu malaman sun tafi akan cewa : zai kalleta a kayan da
take sawa a cikin gida, ta fuskace shi ya kalle ta, sannan ta
juya baya ya kalleta.
Wannan ra'ayin shi ne ya fi dacewa, saboda ta haka mutum
zai san yanayin matar da zai aura.
Ta hanyar bayanan da suka gabata, za mu iya fahimtar cewa
aikin dalilin aure ya hallata, amma da sharuda, ga wasu daga
ciki :
1. Ya zama hoton ya fito da asalin fuskar matar, bai
KWARZANTA ta ba, ta yadda za'a iya yaudarar namijin, ko a
rude shi.
2. Ya zama wacce za'a bawa hoton mai amana ce, ta yadda
ba za ta nunawa wanda ba shi da nufin aure ba, saboda asali
ya haramta ayi kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai
15
in akwai lalura, sai ga wanda yake nufin aurarta, wannnan
yana nuna cewa, bai halatta asa irin wannan hoton na neman
aure ba , a face book, ko a jarida.
3. Ka da hoton ya kun shi fito da tsaraici, ya wajaba a tsaya a
iya inda shari'a ta bada umarni.
4. Zai fi dacewa ace mace ce za ta yii dalilin aure, saboda in
namiji ne, zai iya fitinuwa da hotunan da yake gani, sai barna
ta auku, don haka ita ma macen ya wajaba ta ji tsoron Allah a
cikin aikinta.
Allah shi ne ma fi sani.
25-12-2014
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
NI
Tambaya :
Malam mijina ya sake ni, bayan na yi tsarki daya, sai rikici ya
kaure tsakanin arna da musulmai a garinmu, sai wani christa,
ya dauke ni ya yi zina da ni, yanzu malam yaya zan yi game
da idda ta?
Amsa :
To 'yar'uwa ina rokon Allah ya kawowa musulmi dauki a
Nigeria, wannan mas'alar ta ki malamai sun yi sabani
akanta, akwai malaman da suka tafi akan dole sai kin yi
istibra'i bayan kin gama idda, saidai maganar da tafi zama
daidai ita ce : kawai za ki karasa iddarki ne, ba sai kin yi
istibra'i ba bayan kin kammala, saboda babbar manufar
istibra'i ita ce kubutar mahaifa, hakan kuma zai tabbata idan
16
kika karasa jinane biyun da suka rage miki na iddarki. Yana
daga cikin saukin addinin musulunci kasancewar duk
ibadojin da za su iya shiga cikin juna kuma manufarsu daya
ce, jinsinsu guda ne, to daya za ta shiga cikin daya, kamar
wacce ta yi jima'i sai kuma haila ta zo mata, wanka guda
daya ya ishe ta a karshen hailarta.
Domin neman karin bayani duba: Majmu'ul fawa'id na Sa'ady
shafi na: 141.
Allah ne mafi sani.
25-12-2014
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
17
ba ne sai bayan ta kammala idda, to ba za'a gaskata shi ba,
sai ya kawo shaidu, wadanda za su tabbatar da faruwar
hakan. Yana daga cikin ka'idojin sharia toshe duk hanyar da
za ta kai zuwa barna, idan aka bar abin a bude, wanda yake
kin matarsa, zai iya mata mugunta, ta wannan hanyar, hakan
yasa malamai suka ce sai ya kawo shaidu za'a gaskata shi,
idan kuma bai kawo ba za ta iya zuwa ta yi auranta . Saidai
wasu malaman suna cewa : idan har matar ta gaskata shi, to
ya isa, ko da bai kawo shaidu ba . Duba: Al-mabsud 2\23 da
Mawahibul-jalil 5/408
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
25-12-2014
UKU
Tambaya :
Sheik shin dole ga matar da mijinta ya yi mata shika uku sai
ta yi jini uku, ko idan ta yi jini daya ya yi, tun da babu kome?
Amsa :
To dan'uwa Mazhabar dukkan manyan malaman fiqhu shi ne
za ta yi jini uku ne, ko tsarki uku, saboda fadin Allah a cikin
suratul Bakara aya ta : 228 "Kuma matan aka saka, to za su
jira tsawon jinane uku", wannan ayar ba ta bambance
tsakanin matar aka saka shika daya ba, da wacce aka saka
saki uku, don haka sai hukuncin ya zama daya, Jassas yana
cewa babu sabani a cikin hakan.
18
Saidai Ibnu Taimiyya ya hakaito wani kauli wanda yake cewa:
za ta yi jini daya ne tun da babu kome, saboda an shar'anta
yin jini uku ne don tsawaitawa miji lokacin yin kome, tun da
kubutar mahaifa tana tabbata da yin jini daya. Wannan kaulin
ya sabawa zahirin ayar da ta gabata, sannan kasancewar
iddar matar da mijinta ya mutu wata hudu da kwana goma,
yana nuna cewa, ba saboda tsawaita lokacin kome kawai aka
shar'anta idda ba, tun da ita babu wanda zai mata kome.
Don neman karin bayani duba: Ahkamul-qur'an na Jassas
2/67, da kuma Ahkamul-qur'an na Ibunl-araby 1/185 da
Majmu'ul fatawaa 32\342.
29-12-2014
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
19
ba, wajan hada wani shiri da za ta gabatar, wanda hakan zai
iya kaiwa zuwa barna, domin duk lokacin da mace take
kadaita da namiji to Shaidan zai iya shiga tsakaninsu.
Lalura tana iya halatta abin da yake haramun, saidai anan
wurin babu lalurar saboda za ta iya samun wani aikin na
daban wanda za ta tallafawa rayurwarta da shi, sannan maza
za su iya gamsarwa wajan aikin jarida, ta yadda zai zama, ko
da mata ba su shiga ba, aikin zai ta fi daidai. Aikin Jarida a
gidan talabishin hanya ce da wani zai iya ganin matar aure ya
yi sha'awarta, saboda duk wacce take gabatar da shirye-
shirye dole ta yi kwalliya, wanda hakan zai iya kaiwa zuwa
barna, ka ga sai ya zama haramun.
Malamai suna cewa : Duk lokacin da aka samu aikin jarida
mai tsafta wanda bai sabawa ka'idojin sharia ba, to ya hallata
mace ta yi, saboda duk hukuncin da aka haramta shi saboda
wata illa, yana zama halal idan ta gushe, saidai da kamar
wuya a samu hakan a irin kasashen da ba'a aiki da shari'ar
musulunci, wannan yasa barin aikin ga mace shi ne daidai,
musamman na talabishin wanda ya kunshi barna mafi gima,
kamar yadda bayani ya gabata. Allah ne mafi sani Don
neman Karin bayani duba : Al-mar'atu Almuslima Almu'asirah
na Ahmad Ba-badin shafi na : 429.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
4/2/2015
20
17. TSAKANIN KAFIRI DA MACE MUSULMA, WA ZAN
ZABA?
Tambaya:
Assalamu Alaikum. Na karanta post din da kayi akan
Shugabancin Mata, inda ka nuna bai halatta mace ta yi
shugabanci ba in ba na gidanta ba, Ina so ka dan yi mana
Karin bayani idan aka samu takarar shugabanci tsakanin
Kafiri da kuma Mace Musulma, wanne ya kamata mutane su
zaba a matsayin Shugaba?
Amsa :
To dan'uwa amsa wannan tambayar yana da wahala,
saboda ban ga littafin da ya tattauna mas'alar ba, amma dai
na nemi taimakon Amsa tambayar wajan babban
malaminmu Prof. Muhd Sa'ad Al-yuby, don haka ga bin da zan
iya cewa: Farko dai zaben kafiri haramun ne, saboda fadin
Allah madaukakin sarki "Kuma Allah bai sanya wata hanya ba
ga kafirai akan muminai" Nisa'i aya ta : 141, hakan sai ya
nuna bai halatta musulmai su sanya kafiri ya mulke su ba,
Kamar yadda zaben mace a matsayin shugaba shi ma
haramun ne saboda hadisin Abu-bakrah inda Annabi s.a.w.
yake cewa ; "Duk mutanen da suka sanya mace ta zama
shugabarsu, to ba za su rabauta ba" kamar yadda Bukhari ya
rawaito shi a hadisi mai lamba ta: 4425, Ibnul-kayyim yana
cewa: kore rabauta dalili ne da yake nuna haramcin abu.
Bada'i'ul-fawa'id 4/812.
Saidai kamar yadda malaman shari'a suke cewa: duk lokacin
da abubuwa biyu haramtattu suka hadu, ya zama dole sai an
21
aikata daya daga ciki, to sai a dauki wanda ya fi saukin
haramci a aikata. Idan muka kalli manufar shugabanci a
musulunci, za mu ga ta kunshi: jagorancin mutane da kuma
tsayar da addini, wannan manufar za ta fi tabbatuwa idan
aka zabi mace musulma, fiye da kafiri Crister. Don haka
mutukar matar tana da kokari wajan addini, to ita ya fi
kamata a zaba, ba don kasancewar ya halatta a zabe ta ba,
sai don kawai hakan ya fi saukin haramci, kuma babu yadda
za'a yi a zauna babu shugaba.
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
March 2015
23
kunci a cikin addini ba" Suratu Hajj 78. Don neman Karin
bayani duba Almugni na Ibnu Khudaamah 1/214.
Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
22/2/2015
20. JINI YA ZO MIN, BAYAN CIKINA YA KAI WATA
BIYU
Tambaya:
Assalamu alaikum, malam ya kokari malam tambayace
gareni, na yi wata biyu ban ga al'ada ba, sai yanzu ta rinka
zuwa tana daukewa, na zo asibiti sun ce juna biyu ne, to
inyazo min da safe shikenan sai ya dauke sai kuma gobe da
safe, sai in ya dauke inyi wanka in cigaba da sallah, malam to
ko ya halatta hakan?
Amsa:
To yar'uwa wannan jinin da kika gani mutukar yana kama da
jinin hailar da kaki saba gani, to zai hana sallah, kuma zai
dauki dukkan hukunce-hukuncen jinin haila, saboda asali duk
jinin da ya zowa mace ana daukarsa a jinin haila, in dai ba
akwai wani sababi da zai hana shi ya zama haila ba, kuma
babu wani dalili a alqur’ani ko a sunna da zai hana shi ya
zama haila.
A zance mafi inganci mai ciki tana iya yin haila, don haka duk
yinin da ki ga jini to yana daukar hukuncin jinin haila ne ,
haka ma tsarki yana daukar hukunce-hukuncen tsarki, ta
yadda za ki yi wanka duk yinin da ba ki ga jini ba, Saidai idan
yana yayyankewa kusa-kusa, to kina iya jinkirta wankan, sai
ki hada sallolin da ba ki ga jini ba a lokutansu, saboda yin
wanka a kowanne lokaci akwai wahala a ciki, kuma Allah
24
yana cewa : "Bai sanya muku kunci a cikin addini ba" Suratu
Hajj 78. Don neman Karin bayani duba Almugni na Ibnu
Khudaamah 1\214 da Dima'uddabi'iyya shafi na 11
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
26/2/2015
26
mijinta da bai damu da sallah ba, ko da kuwa lokacin
Ramdahana ne, sannan kuma yana tilasta mata ya sadu da
ita a lokacin watan Ramdhana da rana, bayan haka yana
saduwa da ita tana jinin haila, kuma ta fada masa haramun
ne amma ya ki ya daina, shin malam za ta iya neman saki
tun da ba ya bin dokokin Allah ko ta cigaba da zama da shi?
na gode Allah ya karawa malam basira da hazaka.
Amsa :
To 'yar'uwa mutukar an yi masa nasiha bai bari ba, to za ki
iya neman saki, saboda duk wanda ba ya sallah kafiri ne a
zance mafi inganci, kamar yadda Annabi s.a.w. ya fada a
hadisin da Muslim ya rawaito mai lamba ta: 81. Ga shi kuma
aya: 10 a suratul Mumtahanah ta tabbatar da rashin halaccin
musulma ga kafiri, kin ga cigaba da zamanku akwai matsala
a addinance. Allah ya hana saduwa da mace mai haila a
suratul Bakara ayata: 222, Saduwa da mace da rana a
Ramadana babban zunubi ne kamar yadda hadisin Bukhari
mai lamba ta: 616 ya tabbatar da hakan. Saidai zunubin barin
sallah shi kadai ya isa ya raba aure, idan har bai sake ki ba,
za ki iya kai shi kotu, alkali ya rabaku. Don neman Karin
bayani duba Al-minhajj na Nawawy 2\69.
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
6/3/2015
23. ZAN AURI KANWAR MATAR MAHAIFINA, KO
YA HALATTA?
Tambaya:
27
Malam ya halata mahaifina ya aure mace, ni kuma na auri
kanwarta.
Amsa:
To dan'uwa ya halatta ka aureta, saboda ba ta cikin mataye
guda goma sha biyar wadanda Allah ya haramta a aure su a
cikin suratun-nisa'ai, ga shi kuma babu wani hadisin da ya
haramta a aure ta, Allah yana cewa a cikin suratunnisa'i aya
ta: 24, bayan ya ambaci matan da aka haramta a aura, "Duk
matan da ba wadannan ba, to an halatta muku ku aure su.
Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
10/3/2015
28
Akan iya samun wasu matan 'yan kadan wadanda suke iya
haihuwa ko da ba su taba yin haila ba, saboda Allah mai iko
ne akan komai. Abin da nake ba ka shawara shi ne ku je
wajan likitoci, don su gwada ta, in har suka tabbatar ba za ta
iya haihuwa ba, kana iya hakura da auranta, saboda haihuwa
ginshiki ne, daga cikin ginshikan da suke sa ayi aure. Rashin
yin haila ba falala ba ce, saboda hadisi ya tabbatar da cewa :
"Haila jini ne da Allah ya hukuntawa dukkan 'ya'yan nana
Hauwa'u da jikokinta" kamar yadda Bukhari ya rawaito a
hadisi mai lamba : 290. Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Zarewa
11/3/2015
29
Baihaky ya rawaito shi a Sunan din shi, hakan nan Shafi'i a
Musnad dinsa da sanadi mai kyau, Almajmu'u (4/187).
Haka nan an rawaito cewa Annabi s.a.w. ya sanyawa Ummu-
waraka ladani, sannan ya umarce ta da ta yiwa matan
gidansu limanci, kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi
mai lamba ta : 491, kuma Albani ya kyautata shi.
Bisa dalilan da suka gabata za ki iya yiwa matan unguwarku
limanci, tun da kin fi su karatu, Annabi s.aw. yana cewa:
"Wanda ya fi iya karatun alqur'ani shi ne zai yi limanci"
Muslim 1078. Idan za ki yi musu limanci za ki tsaya ne a
tsakiyarsu in suna da yawa, in kuma ita kadaice sai ta tsaya a
damarki.
Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
13\3\2015
26. NA SADU DA IYALINA, INA AZUMIN NAFILA!
Tambaya :
Salam malam ina hukuncin wadda yana azumin nafila, sai
sha'awa ta zo mai sai ya karya kuma ya sadu da matarsa?
Amsa:
To dan'uwa malamai sun yi sabani game da wanda ya sadu
da matarsa, alhalin yana azumin nafila, akwai wadanda suka
ce sai ya sake, saboda ya bata aikinsa wanda ya faro, kuma
Allah yana cewa: "Kada ku bata ayyukanku" Muhammad aya
ta: 33.
Akwai malaman suka tafi akan cewa ba zai sake azumin ba,
kuma ba shi da laifi. Wannan maganar ta karshe, ita ce
daidai, saboda Annabi s.a.w. yana cewa: "Mai azumin nafila
30
sarkin kansa ne, in ya ga dama ya cigaba da azumi, in ya ga
dama kuma ya karya" Albani ya inganta shi a sahihul-jami'i
hadisi mai lamba ta: 3854. Wannan hadisin sai ya nuna ba shi
da laifi idan ya karya, karya azumi yana tabbata da cin abinci
ko abin sha, ko jima'i, Don neman Karin bayani duba Tuhfatul-
ahwazy 3/356.
Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
16/3/2015
BUDURWATA ?
Tambaya:
Malam ko ya halatta in kalli gashin macen da nike so in aura?
Ko kuma don Allah malam ka taimaka kaman bayanin abunda
ya halatta in kalla a jikin macen da zan aura kafin muyi aure.
Na gode. Allah ya gafarta maka.
Amsa :
To dan'uwa ya halatta ka kalli macen da kake so ka aura,
kamar yadda ya zo a cikin hadisi, inda Annabi s.a.w. yake
cewa : "Idan dayanku yana neman aure, to in ya sami damar
kallon abin da zai kira shi zuwa aurenta, to ya aikata hakan"
Abu dawud a hadisi mai lamba ta : 2082. Malamai sun yi
sabani akan wurin da ya kamata mutum ya kalla a jikin mace
lokacin da ya je neman aure :
1. Akwai wadanda suka ce zai kalli fuska da tafin hannu ne
kawai, saboda tafin hannu yana nuna ni'imar jikin mace,
31
kamar yadda fuska take nuna kyau, don haka sai a takaita
akan su, wannan ita ce maganar mafi yawan malamai. 2.
2. Zai kalli duk abin yake bayyana a jikin mace, don haka
bayan fuska da hannu zai iya kallon duga-dugai da wuya.
3. Wasu malaman sun tafi akan cewa : zai kalleta a kayan da
take sawa a cikin gida, ta fuskace shi ya kalle ta, sannan ta
juya baya ya kalleta. Wannan ra'ayin shi ne ya fi dacewa,
saboda ta haka mutum zai san yanayin matar da zai aura,
yadda ya kamata. Saidai ba'a son yawaita kallon saboda
duk abin da aka halatta saboda bukata, to ya wajaba a
tsaya a gwargwadonta, wannan yasa yawaita zuwa zance
da yawaita yin waya, zai iya zama haramun saboda yana
iya tayar da sha'awa, sha'awa tana iya kaiwa zuwa barna.
Don neman Karin bayani, duba: Al'insaf 8/15 da Muhallah
9/161.
Allah ne mafi sani
Jamilu Zarewa
21/3/2015
32
akan gabatar da na bayi, saboda shi Allah mawadaci ne.
Sannan za ta iya hallaka idan ka bar ta ba ka je ba, sallar
jam'i kuma akwai sabani akan wajabjinta, ga shi kuma za ka
iya gamawa ka dawo kafin lokacinta ya fita, yana daga cikin
ka'idojin sharia, duk abin da ake bukatarsa yanzu-yanzu akan
gabatar da shi akan wanda za'a iya jinkirtawa, ko da bai kai
shi daraja ba.
Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
22/3/2015
33
adda'imah 15\41, da Fataawaa Islamiyya na Ibnu-uthaimin
2/401.
Idan ya zama abin da ma'aikacin banki yake amsa haramun
ne, kuma ba shi da wata sana'a sai wannan, akwai hadari a
auransa, saboda zai ciyar da matarsa da haramun Malamai
suna cewa duk mutumin da yake samun kudi ta hanyoyin
halal da haram, idan ya maka kyauta za ka iya amsa, saboda
Annabi s.a.w. ya yi mu'amala da yahudawa, kuma a
dukiyarsu akwai halal da haram, amma in ba shi da wata
sana'a sai ta hanyar haram to ba za ka iya cin dukiyarsa ba.
Wasu malaman sun halatta aikin banki a bankuna masu kudin
ruwa da niyyar kawo gyara, idan niyyar mutum ta tsarkaka.
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
10\4\2015
35
Malamai suna cewa waiwaye a sallah makaruhi ne saboda
hadisin da ya gabata. Waiwaye yana halatta idan akwai
bukata, saboda akwai lokacin da sayyidina Abubakar ya fara
limanci, saboda Annabi s.a.w. baya nan, bayan Annabi s.a.w.
ya dawo sai ya shigo masallaci, sahabbai suna ganinsa sai
suka fara tafi, sai sayyadina Abubakar ya waiga lokacin da ya
ji tafi ya yi yawa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi
mai lamba ta : 2544.
Malamai suna cewa : waiwayan da Abubakar ya yi yana nuna
hallacin yin waiwaye saboda bukata, tun da Annabi s.a.w. bai
masa inkari ba. Don neman karin bayani duba : Fataawaa
nurun Aladdarb 9/225.
A bisa abin da ya gabata, ya hallata ki dinga yin waiwaye
saboda zubar da yawun da ya zama lalura, saidai duk abin da
aka halatta saboda bukata, ba'a so a wuce gwargwadonta .
Allah ne mafi sani .
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
19/4/2015
36
iya karawa? sai Annabi s.aw. ya ce mata : A'a, saboda an
la'anci masu kara gashi" Bukhari ne ya rawaito a hadisi mai
lamba ta: 4831 .
Hadisin da ya gabata, yana nuna cewa : bai halatta mace ta
kara gashi ba, ko da kuwa mijinta ne ya umarceta, saboda
hakan zai sa ta shiga tsinuwar Allah .
Allah ne mafi sani .
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
22/4/2015
37
Karin bayani duba : Al-mabsud 10\153 da Majmu'ul fataawa
22/114 .
Allah ne ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
27\4\2015
38
maganganun malamai, amma tun da ba ta auri wani ba, ya
wajaba ku hakurewa juna.
Don neman Karin bayani duba : Al-mugni na Ibnu-Khudaamah
7/388 .
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
3/5/2015
40
kaciya, to wanka ya wajaba" na nuna cewa : al'ada ne yiwa
mata kaciya a zamanin Annabi s.a.w.
Ibnu- Abi-zaid Al-kairawany ya ambata a Risala shafi na : 410,
cewa : yin kaciyar mata mustahabbi ne. Don neman Karin
bayani duba Al-mugni 1\101.
Allah ne mafi sani .
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
12/5/2015
42
haramta saboda fadin Allah “Kar ku jefa kawunanku a cikin
halaka” suratu Albakarah aya ta 1952.
Saidai duk da cewa hakan ya halatta da sharudan da suka
gabata, amma barinsa shi ya fi, sai idan bukatar hakan ta
taso, saboda mutum ya zauna akan yadda yake ya fi masa
kwanciyar hankali akan ya yi abin da zai canza dabi’arsa,
musamman ma wasu daga cikin kwayoyin na zamani suna
dagula kwanakin haila, kamar yadda ya bayyana gare mu, sai
a kiyaye.Don neman karin bayani, duba : Dima'uddabi'iyya
shafi na: 54 .
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
22-6-2015
44
cutar, kuma iyalanka su dauka, wannan yasa ba za'a waiga
zuwa damuwarta ba a nan wurin. Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
30/8/2015
45
Tambaya:
Salam malam yayata ta jidda ta ce in tambaye ka menene
hukuncin yin dawafi ga wani, saboda mutane suna yawan
bugowa suna cewa a musu dawafi, kuma ta ce in gaya ma
wai don Allah ka Amsa a facebook, saboda ana bukatar sanin
amsar.
Amsa:
To 'yar'uwa babu wani dalili ingantacce wanda yake inganta
yiwa wani dawafi, sannan kuma ba'a samu magabata na
kwarai suna yi ba, ga shi kuma dawafi ibada ce, ita kuma
ibada ba'a yin ta sai da dalili daga Alqur'ani ko Sunna, amma
dai ana iya yiwa wani addu'a lokacin da mutum yake yiwa
kansa dawafi.
Akwai dalilai da yawa wadanda suke nuna ingancin yiwa
wani Umara ko Hajji, saidai ba'a samu na dawafi a karan
kansa ba.
Kiyasin dawafi akan Hajji da Umara ba zai yiwu ba, saboda
dawafi tsantsar ibadar jiki ce, hajji da umara kuma ibadu ne
da suka hada jiki da dukiya, duk ibadar da ta hada jiki da
dukiya, tana Amsar wakilci, amma wacce ake yin ta da jiki
kawai ba ta Amsar wakilci kamar sallah.
Allah ne mafi Sani
7-9-2015
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
46
Assalamu alaikum, shin ko ya halatta ga matar Aure ta yi
facebook, harma da charting?
Amsa : Wa alaikum assalam Wannan tambaya ce mai
wahala. Saidai abin da zance duk abin da zai amfane ta za ta
iya yi a face book, saboda asali a shari'ar musulunci, duk abin
da mutane suke aikatawa a mu'amalarsu ta yau da kullum
halal ne, mutukar ba'a samu wani nassi wanda ya haramta
ba, ko kuma ya kasance cuta tsantsa, haka ma idan mafi
rinjayansa barna ne, ka ga face book kuwa babu wani nassi
da ya haramta shi, sannan ba cuta ba ne tsantsa, tun da ana
iya samun ilimin addini ta wannan kafa. Ya kamata ta daina
yin charting da wadanda da muharramanta ba in ba malamin
da ta yadda da iliminsa da tsantseninsa ba, za ta yi masa
fatawa, saboda akwai maza da yawa da suke bi ta hanyar
charting don lalata matan auren da ba su da kamewa.
Wannan ya sa barin charting da mazan da ba muharramai ba,
ko kuma wadanda suke neman auran matar, zai iya zama
wajibi, saboda hakan yana kaiwa zuwa barna, duk abin da
yake kaiwa zuwa barna, zai iya zama haramun ko makaruhi,
kamar yadda malaman musulunci suka tabbatar.
Allah ne mafi sani
29-9-2015
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
47
Amsa:
To dan'uwa wasu daga cikin malamai sun karhanta auran
mata biyu a yini daya, saboda hakan zai kawo matsala wajan
bawa matan hakkinsu na kwana, saboda duk wacce aka fara
da ita, to dayar za ta cutu, saidai idan hakan ta faru, to zai
fara ne da wacce ta fara shigowa gidan, in kuma sun shigo
tare ne sai ya yi musu kuria. Don neman Karin bayani duba :
Al-kafy Na Ibnu Khudaamah shafi na: 981. Allah ne ma fi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
5/10/2015
46. FATAWAR NAN AKWAI GYARA
Malam fatawarka da ka yi akan mijin da matarsa ta neme shi
da jima'i, bai amsa mata ba, ba shi da laifi, mun watsa ta a
group da yawa, kuma ta hadu da kalubale, ga abin da wata
take cewa: Nake ganin idan har aka ce namiji kawai ne zai
iya kusantar matarsa duk lokacin da ya so ko tana so ko ba
ta so, ita mace idan ta nemi hakan ko bai biya ma ta
buqatarta ba sai lokacin da ya so, Anya akwai adalci a
hakan? Idan akwai istidlali naqli a taimakamin da su ba aqali
ba. Na ga istidlal din na aqali aka kawo a rubutun.
Ya za'ayi mace ta nemi mijinta ya qi amince ma ta, duk da
kasancewar mace tana da kunya. Amma har ta iya nemansa
ka ga kuwa akwai dalilin da ya sa ta neme shi. Ai shi ma
namiji ko da bai da sha'awa da an taba shi sha'awarshi za ta
motsa. Kenan hakan ba zai zamo dalili da zai sa don mace ta
nemi mijinta ba ya ki amincewa da dalilin wai baya da
sha'awa.
Amsa:
To abin da zan iya cewa shi ne: saduwar da muke magana
akanta ibada ce, ibada kuma tana bukatar dalili kafin a
tabbatar da ita, babu wani dalili Wanda ya wajabtawa miji
48
amsa kiran matarsa duk lokacin da ta neme shi, sannan
yanayi da al'ada ya tabbatar da cewa namiji ba zai iya
saduwa da mace ba duk lokacin da ta name shi, saboda
Namiji yana bukatar nashadi kafin saduwa, sabanin mace,
wacce take a matsayin katifa, wannan yasa malamai da
yawa na sharia suka tafi akan cewa ba'a yiwa namiji fyade,
tun da in azzakarinsa bai motsa ba, ba zai sadu da mace ba,
mace kuwa an cimma daidaito za'a iya mata fyade saboda
kamar tirmi take, in har an samu tabarya shike nan, wannan
yasa za'a iya saduwa da mace tana bacci sabanin namiji.
Kasancewar an ce babu la'anta akansa idan matarsa ta
neme shi bai amsa mata ba, ba ya nuna ya halatta ya cutar
da ita, yaki saduwa da ita a lokacin da yake da nishadi. Allah
ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
14/10/2015
49
Malamai sun yi ijma'i akan haramcin zubar da ciki bayan an
busa masa rai, saboda ya zama kashe rai ba da hakki ba.
Amma sun yi sabani game da zubar da ciki kafin ya kai
watanni hudu, wasu sun haramta, wasu sun halatta wasu
kuma sun karhanta.
Amma abin da yake daidai shi ne ya halatta a zubar da cikin
da bai kai wata hudu ba, idan akwai lalura, zubar da cikin
Sikila ba dole ya zama lalura ba, tun da ana iya haihuwarsa
ya rayu, ya bautawa Allah ya amfani al'uma, don haka barin
cikin shi ne ya fi, saidai idan kuka zubar kafin ya cika wata
hudu saboda matsalar da kuke tunanin yaron zai iya
fuskanta a rayuwarsa, ba za'a ce kun yi laifi ba, tun da bai
zama mutum ba, kuma ba za'a tashe shi ranar alkiyama ba.
Don neman karin bayani duba Ahkamu al-janin fil-fiqhil
islamy na Umar Ganam Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
18/10/2015
50
abin, malam matsalar anan shi ne matar tace ya saketa
amma shi yace bai sake tava , Allah ya san zuciyar shi , idan
harta dawo mashi da wannan abun ,to ya warware kalamin
sakin da yayi, matar ta tsayu akan saki ne amma shi yace ba
sakine va, Mallam don Allah menene gaskiyar wannan lamari
? Allah yasaka da alkhairi amin.
Amsa: Abin da yake daidai shi ne saki ne, saboda niyya ba
ta da tasiri a saki,
ana amfani ne da Abin da miji ya furta. Ya rataya sakin da
wani abu, kuma abin ya tabbata, ya kuma zo ya furta, don
haka ta saku. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
20/10/2015
51
31/10/2015
53
53. ZAN IYA YIWA MATATA KOME, BAYAN TA FARA JINI
NA UKU?
Tambaya:
Malam idan mace tana iddah Har tana Kan jini na uku. miji
zai iya maida ta?
Amsa:
To Dan'uwa Allah yana cewa a suratul Bakara aya ta: 228,
"Kuma matan da aka şaki, za su jira (kur'i) uku kafin su gama
idda", saidai Malamai sun yi sabani game da ma'anar (kur'i)
a ayar.
A wajan malaman Malikiyya kur'i a ayar yana nufin tsarki,
don haka duk matar da aka saka in dai ta shiga jini na uku to
miji ba shi da damar yi mata kome, saboda za'a sake ta ne a
tsarki sai ta yi jini sai tsarki, sai jini sai tsarki, daga ta shiga
jini na uku za ta zama ta kammala iddarta.
Malaman Hanafiyya sun fassara (Kur'i) a waccar ayar da jini,
don haka mutukar ba ta kammala jini na uku ba, to miji zai
iya mata kome, Tunda zata fara idda ne da jini, don haka ba
zata kammalaba sai a karshen jini na uku.
Wasu Malaman suna inganta Mazahabar Hanafiyya saboda
Annabi s.a.w ya kira haila da sunan Kur' i a hadisin Imamu
Ahmad mai lamba ta: 25681
Don neman karin bayani duba: Tafsirin Ibnu-Kathir 1/607.
Allah ne mafi Sani.
Dr.Jamilu Zarewa
8/11/2015
54. ZAN IYA SADUWA DA MAI HAILA, IDAN NA SANYA
CONDOM?
Tambaya: Salam. Malam Allah ya karama daukaka da imani.
Shin mutum
54
zai iya saduwa da matarsa idan tana Haila matukar yasa
Condom?
Amsa:
To dan'uwa bai halatta ka sadu da mai haila ba ko da kuwa
ka sanya Condum, saboda Allah ya haramta saduwa da mai
haila, kuma ya kira jinin haila a aya ta 222 a suratul. Bakara
da cuta, sannan ya rataya halaccin saduwa da mace mai
haila da abubuwa biyu wato: yankewar jini da kuma yın
wanka. Ba namiji ne kadai haila take iya cutarwa ba, idan
ana saduwa da mace mai haila mahaifarta za ta takure sai
jini ya barke mata, wannan sai yake nuna cewa: ba za'a sadu
da mace mai haila ba ko da an sa Condum .
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Zarewa
28/11/2015
56
Dr. Jamilu Zarewa
2/12/2015
58
Malam wata mace ce ta yi bakance za ta yi azumin Annabi
Dawud, wato yau ta yi azumi gobe ta sha, amma kuma yanzu
ta yi aure ta kasa, ya ya kamata ta yi ? shin akwai mafita ?
Amsa :
To dan'uwa Bakance makaruhi ne, haramun ne a wajan wasu
malaman, saboda Annabi s.aw yana cewa : "Bakance ba ya
zuwa da alkairi" kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai
lamba ta : 1639. Saidai ya wajaba a cika bakance idan aka yi.
Wasu daga cikin malaman hadisi sun ta fi akan cewa idan
mutum ya yi bakance ya kasa cikawa zai iya yin kaffarar
rantsuwa, saboda hadisin da aka rawaito daga Muslim a
lamba ta: 1645 a sahihinsa, wanda Annabi s.a.w. yake cewa :
"Kaffarar bakance irin kaffarar rantsuwa ce" . Duba Alminhaaj
na Nawawy 4/269
A bisa abin da ya gabata za ki iya yin kaffarar rantsuwa wato:
ciyar da miskinai goma, ko tufatar da su, ko kuma 'yanta
kuyanga, idan babu hali, sai ayi azumi uku, kamar yadda ya
zo a suratul Ma'idah aya ta : 89 .
Allah ne ma fi sani
Dr. Jamilu Zarewa
12\7\2015
62. WANDA YAKE GIDA, ZAI IYA HADA SALLOLI
SABODA RUWAN SAMA ?
Tambaya:
Assalamu alaikum. Allah karawa malam ilimi da fahimta.
Shin da Allah malam ko mutum zai iya hada sallah shi kadai
idan ana ruwa bashi da ikon zuwa masallaci? Nagode malam
Amsa:
59
To dan'uwa malamai sun yi sabani akan wannan mas'alar
zuwa maganganu guda biyu :
1. Ya halatta ga wanda yake a gida ya hada salloli saboda
ruwan sama, tun da ruhusa ce Allah ya bawa mutane, don
haka ta shafi kowa da kowa, wannan ita ce maganar
Hanabila kamar yadda Mardawy ya ambata a INSAAF 2\340.
2. Bai halatta ga wanda bai je sallar jam'i ba ya hada salloli
saboda ruwan sama, saboda an yi sauki ne ga wadanda za
su je masallaci don kar su jika jikinsu da ruwa, wannan
wahalar kuma babu ita ga wanda ya yi sallah a gida, don
haka rahusar ba za ta same shi ba, sannan kuma shari'a ta yi
nufin ta kiyaye sallar jam'i shi ya sa ta saukaka wajan hada
salloli a ruwan sama,don kar mutane su watse sallar jam'i ta
tozarta, wannan ita ce maganar Imamu shafi'i a littafinsa
Al'umm 1\195 A fahimtata maganar karshe ta fi inganci, don
haka wanda yake gida ba zai hada salloli ba. Allah ne mafi
sani
Dr. Jamilu Zarewa
9/11/2015
61
64. INA YAWAN WAYA DA BURDURWATA, KO YA
HALATTA A SHARI'ANCE?
Tambaya: Dan Allah ina tambaya, Namiji ne yakeso ya qara
aure to shine bayan ya dawo gida da dare sai budurwar ta
riqa kiran shi ko kuma ta riqa turo txt, shikuma idan matarshi
tana kusa sai ya riqa avoiding amma da ta dan daga sai
shima ya fara responding ko ya kira ta, kuma idan asuba tayi
sai ta kirashi. To shine matar ba taso, dan Allah a Shari'ance
yana da laifi ko ba shi da? sannan matar zata iya neman ya
dena ko kuwa ta shiga rayuwarsa ne a shari'ance?
Amsa:
To dan'uwa yana da kyau ka san cewa matar da kake nema
aure ba muharramarka ba ce, don haka bai halatta ka dinga
hira da ita ba, sai gwargwadon bukata.
Yawan hira da budurwa da jin dadin zancenta, yana daga
cikin abubuwan da suke kaiwa zuwa ga fitina, mai AHLARI ya
kirga jin dadin zancen wacce ba muharrama ba daga cikin
ayyukan da Allah ya hana.
Duk wanda yake yawan hira da matar da ba muharramarsa
ba, yana jin dadin zancenta, Allah zai iya haramta masa jin
dadin zancen matarsa ta halal.
Ya wajaba hirarka da buduwarka ta zama gwargwadon
bukata, saboda jin dadin zancenta, zai iya kai ku, ku aikata
katon sabo, yana daga cikin ka'idojin shari'a toshe duk
hanyar da take kaiwa zuwa barna. Zunubi shi ne abin da ya
sosu a ranka kuma ka ji tsoron kar mutane su yi tsinkayo,
kamar yadda hakan ya tabbata a hadisin Muslim mai lamba
ta: 2553.
62
Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
4/1/2016.
63
66. ANGO YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA
BATUN GADO DA TAKABA?
Tambaya:
Assalam pls. an daura auren wasu yau ba'a dauko amarya ba
sai gobe, amma Allah yayi wa angon rasuwa, tambayata
anan wai shin za tayi takaba? Kuma tanada gadonshi ?
Amsa: To dan'uwa idan miji ya mutu bayan an daura aure
kafin ya tare da amaryarsa, ya wajaba amaryarsa ta yi masa
takaba, kuma a bata gadonta cikakke, kamar yadda Annabi
S.a.w. ya yi hukunci da hakan ga Barwa'u 'yar Washik lokacin
da mijinta ya mutu kafin su tare a hadisi mai lamba ta: 1145,
wanda Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi .
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
5\1\2016
67. NA YI WANKAN JANABA, SAI MANIYYI YA SAKE
ZUBO MINI ?
Tambaya:
Assalamu Alaikum tambayata itace idan mata ta sadu da
mijinta tayi wanka immidietly bayan ta gama tana zaune sai
taji sperm ya zubo mata shin zata kara yin wani wanka ko
kuma wanda tayi ya isa ?
Amsa:
Wa alaikum assalam, To idan sabuwar Sha'awa ce ta zo
mata, ta zubar da maniyyi, ya wajaba ta sake wanka, amma
idan saboda saduwar da suka yi ne a baya : za ta wanke
wurin ne, ta sake alwala, amma babu bukatar sake wanka,
wanda ta yi na farko ya isa. Duba Bidayatu Almujtahid 1\48
da Insaf 1/232. Allah ne mafi sani
64
Dr. Jamilu Zarewa
2/1/2016
65
magana da mahaifi saboda Allah ya hana fadawa Uba kalma
mara kyau ko yaya take, kamar yadda ya zo a Suratul Isra'i.
Ba'a son ana yın muguwar addu'a ga iyalai saboda in aka
dace da lokacin amsar addu'a za ta zamar masa matsala
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
16/1/2016
66
Assalamu alaikum,Allah gafarta malam shin zan iya yawo
acikin gida ba dan kwali?
Amsa:
Mace zata iya yawo babu Dan kwali idan tana tsakanin 'yan
uwanta mata musulmai saboda al'aurar mace ga 'yar uwarta
mace musulma tana kasancewa ne tsakanin gwuiwa zuwa
cibiya, mutukar akwai mazan da ba muharramai ba to bai
halatta ta bude kanta ba, saboda dukkan mace Al'ura ce in
ban da fuska da tafukan hannu. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Zarewa
24/1/2016
67
sai an aikata daya daga ciki sai a zabi karama a aikata,
wannan yasa Imamu Ahmad da Ibnu Hazm suka halatta
auran hannu ga wanda ya ji tsoron zina kuma ba shi da halin
da zai yi aure.
Idan mu ka ce auran hannu haramun ne, saidai barnar dake
cikin zina tafi girma, domin zina akwai keta alfarma a ciki,
sannan tana kaiwa ga cakuduwar nasaba, ta yadda za'a haifi
'ya'ya gantalallu, marasa asali, wannan ya sa magana ta
biyu ita ce mafi inganci, mutukar an samu sharudan da suka
gabata. Don neman Karin bayani duba: Muhallah 12\407 da
Majmu'ul fataawaa 34/146. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Zarewa
23\1\2016
68
dauke nayi wanka, to shine akace min sai na Rama wannan
kwanaki goman shima. To malam ya azumin tawa take.
Amsa:
To 'yar'uwa Allah madaukakin sarki a cikin alqur'ani ya
rataya hukuncin jinin haila ne da samuwarsa, don haka
mutukar kin ga jinin haila da siffofinsa (Baki, ko karni) to ya
wajaba ki bar sallah da azumi, har zuwa lokacin da zai
dauke, saidai in ya zarce iyaka ta yadda zai zama, yana zubo
miki a mafi yawan kwanakin rayuwarki ko dukanta, to a
lokacin ne yake zama jinin cuta ta yadda ba zai hana sallah
da azumi ba. Duk da cewa tsara iyali ya halatta saboda
hadisin Jabir wanda yake cewa "Mun kasance muna yin azalo
(zubar da maniyyi a wajen farji yayin saduwa) a lokacin da
Qur'ani yake sauka, kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi
mai lamba ta: 4911, saidai yawancin magungunan tsara iyali
suna birkita al'ada, wannan yasa barin su shi ne ya fi, in ba
likita ne ya tabbatar da lalurar shan ba, ko kuma aka gane
maganin ba ya cutarwa ta hanyar jarrabawa. Allah ne mafi
sa ni
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
22/1/2016
69
honey moon, to meye hukuncin daya matar, ya zalumceta
kenan?
Amsa:
To dan'uwa Anas RA ya rawaito cewa: "Yana daga cikin sunna
In mutum ya auri budurwa kuma yana da wata matar, ya yi
mata kwana bakwai, in kuma bazawara ce kwana uku"
kamar yadda ya zo a Sunanu Attirmizi a hadisi mai lamba ta:
1139, wannan sai ya nuna kari akan haka ya sabawa sunna.
Amma Idan Uwar gida ta bada izni ya halatta ayi kari akan
haka, tun da ya halatta mace ta sarayar da hakkinta na
kwana, kamar yadda Saudatu ta bawa Nana A'isha
kwananta, lokacin da girma ya zo mata, ta ga Annabi s.a.w.
bai damu da ita ba sosai, kamar yadda Bukhari ya rawaito a
hadisi mai lamba ta: 4914, wannan sai ya nuna halaccin
sarayar da hakkin kwana, da yiwuwar yiwa amarya kari idan
uwar gida ta yarda. Allah mafi sani
Dr. Jamilu Zarewa
31/1/2016.
71
mai sauki, babu kunci da damuwa a cikinsa, kamar yadda
aya ta karshe a suratu Al-hajj ta yi bayanin haka.
Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
3\2\2016
72
karyata Allah, wanda ya karyata Ubangiji hukuncinsa a
fili yake.
2. Yana daga cikin akidunsu tabbatar da cewa: Alqur'anin
da yake hannunmu bai cika ba, tare da cewa: Allah ya
tabbatar: zai kiyaye shi, har abada.
3. Rafidha 'yan shia sun tafi akan cewa Nana A'isha
Mazinaciya ce, tare da cewa Allah ya kubutar da ita
daga abin da munafukai suka zarge ta da shi a ayoyi
guda goma a suratun Nur.
Duk da cewa da yawa daga cikin 'yan shi'a suna kore
wadannan aqidu, saidai ayyukansu da littatatafansu da
maganganunssu, suna karyata korewarsu. Shugabansu
Zakzaky yace ba ya zagin sahabbai, kawai sai muka gan shi
a zaune a Husainiyyar Zariya yana la'antarsu, Haka Yakubu
Yahya na Katsina shi ma ya yi ikrarin haka, sai ga shi mun ji
shi yana siffanta Sahabbai da 'yan PDP, yana ci musu
mutunci da cewa sun yi juyin mulki. Ya wajaba ka sani yana
daga cikin manyan aqidun 'Yan shi'a TAKIYYA wato yin karya
ga wanda ba dan shi'a ba, kuma duk wanda bai iya wannan
ba, to bai cika dan shi'a ba a wajansu, domin ginshikin
addininsu ce, don haka kar ka dogara da maganarsa.
Annabi s.a.w. yana cewa : "Idan wanda kuka yarda da
addininsa da dabi'unsa ya zo muku, to ku aura masa" kamar
yadda Tirmizi ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 1084, duk
wanda addininsa ya kunshi abin da ya gabata, bai halatta a
aura masa mace ba, tun da Allah bai yarda da hakan ba,
kuma addininsa ba yardajje ba ne, Allah ya ba ta miji nagari
wanda ba dan shi'a ba. Allah ne mafi Sani.
73
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
6/2/2016.
74
Zina sabon Allah ne da kuma yada fasadi a bayan qasa. Aure
kuwa sunnar Manzon Allah ne, da samar da zuriya mai
albarka. Kuma an kwadaitar da mu yin sa.
Amma Mazhabar Malikiyya suna ganin matar da aka yi zinar
da ita sai ta yi jini wanda ake kira Istibra’i, kafin a daura
mata aure domin a raba maniyyin zinar da na aure. Kuma
idan har an daura aure ba ta yi wannan jinin ba, to, za a raba
wannan auren ko da sun haifi `ya`ya, domin suna ganin an
daura auren ne a cikin idda, kuma Allah Ya hana daura aure
a cikin idda. Saboda haka, a wurinsu, wannan auren batacce
ne kuma rusasshe. Amma Mazhabar Abu Hanifa da Imam
Shafi`i suna ganin macen da ta yi zina, an so ta yi istibra’i
kafin ta yi aure, amma idan har an daura auren ba ta yi
istibra’i ba, auren yana nan daram, ba za a raba su ba. Kuma
suka qara da cewa ko da tana da cikin zinar ne aka daura
mata aure, to auren yana nan. Sai dai Imam Abu Hanifa ya
ce: mijin da ta aura, ba zai sadu da ita ba, har sai bayan ta
haihu, ko da kuwa cikin zinar nasa ne ko na waninsa.
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:
"Duk wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira, to kada ya
shayar da ruwansa ga shukar waninsa" Abu-dawud:1847.
Don neman karin bayani duba: AL-MUDAWWANNAH AL-
KUBRAH 2/173 da Al-mugni na Ibnu-Khudaamah 8/79
A fahimtata, fatawar Malikiyya ta fi inganci kafin ayi auren,
saboda fita daga sabanin malamai abin só ne, sannan kuma
za'a kaucewa fadawa hadari, amma idan an riga an yi auren
to fatawar Hanafiyya abar lura ce, saboda akwai bambanci
75
tsakanin zina da aure, saidai ya wajaba şu nisanci saduwa,
kafin ta haihu Saboda hadisin da ya gabata. Allah ne mafi
sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
27\2\2016
78
dağa Annabi s.a w. yana hada mace da namiji, in ba'a samu
abin da ya kebance shi ba, Tabbas fitsarin mace a tsaye zai
jawo matsala wajan cikar tsarkinta, saboda yanayin halittar
da Allah ya yı mata.
Yana daga cikin Ka'idojin sharia gabatar da wajibi akan abin
da aka halatta, yin fitsari a tsaye ya halatta ga mace, saidai
zai kai ga kunci wajan tabbatar da Dhahara, wacce sallah ba
ta ingantuwa saida ita. Duk hadisan da suka zo cewa Annabi
ya hana yin fitsari a tsaye ba su inganta ba, sai hadisin Nana
A'isha wanda Hakim ya inganta, in da take cewa : "Duk
wanda ya ce muku Annabi s.a.w ya yi fitsari a tsaye kar ku
gaskata shi" kamar yadda Nasa'i ya rawaito a hadisi mai
lamba ta: 29.
Malamai suna cewa : za'a dau maganarta akan tana bada
labari ne, akan abin da ta gani, wannan ba ya kore a samu
wani abin daban wanda ba ta sani ba, tun da ba koyaushe
take zama tare da shi ba, yana daga cikin Ka'idoji a wajan
malaman Usulul-fiqhi : Duk wanda ya tabbatar da abu za'a
gabatar da maganarsa akan wanda ya kore, saboda wanda
ya tabbatar yana da Karin ilimi na musamman wanda ya
buya ga wanda ya kore. Don neman Karin bayani duba :
Sharhu Assuyudy ala Sunani Annasa'I 1\26.Allah ne mafi
sani.
Dr Jamilu Zarewa
8\3\2016
79
Asalamu Alaikum malam ya aiki malam, don Allah ya ka'idar
sallar walaha take ? Allah ya saka da Alheri
Amsa:
To 'yar'uwa sallar walaha ba ta da wani adadin raka'o'i na
musamman, Za ki iya yın raka'a biyu ko hudu ko shida da
sallama uku, mafi yawan abin da aka rawaito daga Annabi
s.a.w. a sallar walaha shi ne raka'a takwas, kamar yadda ya
yi ranar bude Makka, Bukhari ya ambaci kissar a hadisi mai
lamba ta: 5806. Lokacin sallar walaha yana farawa daga
sanda rana ta fara zafi, kamar yadda hadisin Muslim mai
lamba ta: 748 ya tabbatar da hakan, har zuwa dab da
karkatar rana daga tsakiyar sama. Allah ne mafi sani
Dr Jamilu Zarewa
9\3\2016
85. BABU HADISI INGANTACCE AKAN YAWAN
KWANAKIN HAILA!
Tambaya:
Na karanta amsar da malam ya bada wadda ban fahimce
taba, Abisa T
tambayar da akayi mashi. Ta zuwan jini duk sati tare da
cewa taje asibiti Amman sunce saidai tayi hakuri in na
fahimci tambayar. Hukuncin matar da take da irin wannan
lalura shine : Zata bar salla a duk lokacin da jini yazo mata in
lokacin yin al'adattane ko da ya doge harfiye da kwanakin da
takeyi mutukar bewoce kwana(15) ba, Amman in ya woce
haka zatayi wanka tayi salla don haila ba ta wuce kwana(15).
Amsa:
80
Abin da abokina ya fada shi ne fatawar Malikiyya da
Shafi'iyya, saidai babu ko hadisi daya da ya tabbata akan
cewa : jinin haila ba ya wuce kwana sha biyar, duk hadisan
da suka zo akan haka ba su inganta ba, daga ciki akwai
hadisin da aka rawaito cewa: "An tambayi Annabi s.a.w
game da tawayar addinin mace, sai ya ce: "Daya daga
cikinsu zata zauna rabin rayuwarta ba ta sallah" Ibnul Jauzu
ya raunana shi a littafinsa Attahkik 1/263 haka Annawawy
shi ma ya ce: hadisin karya ne, kamar yadda ya zo a
AlMajmu''u 2\405, Ibnu Abdulhady shi ma ya raunana shi a
cikin Tankihu attahkiki1\414, Baihaki a cikin Ma'arifatu
assunan wal-athar,2/145 yana cewa: Na nemi hadisin da
sanadi a littattafan hadisi amma ban taba ganinsa ba, Haka
nan Hanafiyya sun tafi akan cewa: Jinin haila ba ya wuce
kwana goma, saidai duk hadisan da suka kafa hujja da su
babu ingantacce a ciki, Duba Al-ilal Al-mutanahiyah na Ibnu
Al-jauzy 2/382.
Zance mafi inganci shi ne haila ba ta da wasu kwanaki na
musamman, kamar yadda sheik Ibnu Uthaimin ya tabbatar
da haka a littafinsa na Dima'uddabi'iyya, tun da Allah da
manzonsa sun rataya hukunce-hukuncenta ne da
samuwarta, don haka duk inda aka samu jinin haila da
sifofinsa (baki, karni) hukuncinta yana tabbata, saidai idan
ya kasance mafi yawan rayuwa ko dukkanta, a lokacin ne zai
zama jinin cuta. Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa
11\3\2016
81
86. MIJINA YA MUTU, TUN KWANA (40), KO ME YA
KAMATA NA YI?
Tambaya:
Asalamu Alaikum malam tambayata maitakaba bayan tayi
kwana Arba’in, in tayi wanka zata iya goga shuwa a
hammatarta?
AMSA:
To Yar'uwa ina rokon Allah ya jikan mijinki, akwai hukunce-
hukunce da suka shafi takaba, ga muhimmai daga ciki:
1. Mai takaba za ta zauna a gidan mijinta ba za ta fita ba,
har sai ta gama iddarta, wacce take wata hudu da
kwana goma, kamar yadda aya ta: 234 a suratul Bakara
take nuni zuwa hakan.
2. Ba za ta saka kaya masu kyau ba, don haka za ta guji
ado, kamar yadda hadisin Abu-dawud mai lamba ta:
2304, ya yi bayanin hakan.
3. Shari'a ta hana mai takaba ta sanya turare, kamar
yadda hadisin Bukhari mai lamba ta: 5343, ya tabbatar
da hakan,
4. Malamai suna cewa mai takaba ba za ta sanya tozali
ba, kamar yadda hadisin Nasa'i mai lamba ta: 3565 ya
bayyana hakan.
5. An hana mai takaba yin lalle, kamar yadda hanin ya zo
a hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304.
6. Idan wata bukata ta kama za ta iya fita daga gida, ko
da rana ne ko da dare.
7. Za ta iya yin Magana da mazan ba muharramanta ba,
idan bukatar hakan ta kama, saidai ta guji, sanyaya
murya, kamar yadda aya ta 32 a suratul-ahzab ta hana
hakan.
82
8. Babu wani launi na kaya na musamman da aka
shar'anta mata ta sanya, don haka, duk kayan da ba
kwalliya a jikinsu ya halatta ta sanya su.
9. Za ta iya yin wanka da sabulun da yake ba mai kanshi
ba.
10. Za ta iya zama ta yi hira da makusantanta, har
ma za ta iya bude gashin kanta, idan duk
muharramanta ne.
11. Ya haramta ga mai takaba ta yi aure, har sai ta
kammala iddarta wata hudu da kwana goma, kamar
yadda aya ta: 235 a suratul Bakara take nuni zuwa
hakan. Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Yusuf Zarewa
15/03/2016
84
takaba fita da rana, kamar yadda Ibnu-khudaama ya ambata
a littafinsa na Mugni 8/130. Duk da cewa wasu malaman
Hadisin sun raunana hadisin Baihaki da ya gabata, saidai an
samu kwatankwacinsa daga maganar Abdullahi dan Mas' ud
da Abdullahi dan Umar Allah ya kara musu yarda, maganar
Sahabi hujja ce, in har ba'a samu wani sahabin ya saba maşa
ba, kamar yadda yake a ilimin Usulul-fiqh. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Zarewa
22/3/2016
89. ZAN IYA KOMAWA WAJAN TSOHON MIJINA, IDAN
NA BIYU YA SAKE NI, KAFIN MU SADU?
Tambaya:
Assalamu Alaikum Malamina. Fatan Alkhairi a gareka, da
fatan ka wuni lafiya cikin koshin lafiya. Malam dan ALLAH ina
da tambaya kamar haka: (Mutum ne ya saki matarsa har
saki (3) a lokuta daban-daban, to, sai wani bawan ALLAH
yazo ya aure, bayan ya aureta sai wata matsala ta shiga
tsakaninsu kuma ya saketa amma kuma ko sau daya bai
taba sadu da ita ba, to, yanzu Malam ko wancen tsohon mijin
nata zai iya mayar da ita, tun da gashi tayi aure amma
saduwace kawai ba'a yi da ita ba??? ALLAH ya kara taimakon
ka Malam.
Amsa:
Wa alaikum assalam, ina har ba su sadu ba, to bai halatta ta
auri wani ba, saboda lokacin da matar Rifa'ata ta auri wani
bayan mijinta ya sake ta, ta so ta rabu da mijinta na biyun,
ta koma wajan na farkon, kafin su sadu, Annabi s.a.w. ya
hanata, inda ya ce mata : "Dole sai kin dandana dadinsa, shi
85
ma ya dandana dadinki, kamar yadda Bukhari ya rawaito a
hadisi mai lamba ta:5372, wannan sai ya nuna cewa aya ta :
230 a Suratul Bakara, ba aure kawai take nufi ba, tana nufin
aure hade da saduwa su ne suke halatta mace ga mijinta na
farko, saboda aikin Annabi s.a.w. da maganarsa su ne suke
fassara Alqur'ani. Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Zarewa.
27/3/2016
86
4/04/2016
Tambaya:
Assalamu Alaikum malam menene hukuncin wadanda sukayi
auran kisan wuta suka maida aurensu,kuma menene
hukuncin auren nasu?
Amsa:
Wa alaikum as salam, Auran kisan wuta bai halatta ba.
Saboda Annabi (S.a.w) ya la'anci wanda ya yi da kuma
wanda aka yi saboda shi, kamar yadda Tirmizy ya rawaito
kuma ya inganta shi. Idan miji ya yi aure da niyyar halattawa
mijin baya, auran batacce ne, amma idan mace ce ta yı da
wannan niyyar, kuma mijin da ta aura bai sani ba, to auran
ya yi. Saboda ba dole ba ne mijin ya sake ta. Yana daga cikin
87
Ka'idojin sharia: من ل فرقة بيده ل أثر في نيتتتهDuk wanda babu
saki a hannunsa, to niyyarsa ba ta da tasiri.
Allah ne mafi sani
Dr jamilu Zarewa.
29/3/2016
88
ta iya sanyawa a tsakanin 'yan'uwanta mata, ko gaban
muharramanta wadanda ta san ba za su yi sha'awarta ba.
Dr Jamilu Yusuf Zarewa
31/03/2016
90
saboda in kin yi haka za ki fita daga kokwanto, kuma zai
zama tabbas kin rama abin da ake binki, ki rama abin da za
ki nutsu a zuciyarki kin rama. Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa.
18/04/2016
91
kafin ta gama, Ba'a idda da watanni uku sai ga wacce ba ta
fara haila ba, ko kuma wacce ta yanke kauna daga haila
saboda tsufa, kamar yadda aya ta: 4 a suratu Addalak ta
tabbatar da hakan. Allah ne mafi Sani.
Dr Jamilu Zarewa
22/04/2016
92
Salamun'alaikum Malam Wai akwai sallah ga wanda in yana
sallah sai ya fitar da iskar tusa kuma duk sallah yake hakan
koda ace yayi kashi kafin yayi sallar, amma in har ya zo
sallah sai ta futo koda ace zayyi alwala sama da 10?
Amsa:
Wa alaikum assalam, akwai sallah akan shi, ba za ta taba
faduwa ba akansa, ya wajaba a gare shi ya yi alwala yayin
kowacce sallah, dağa nan duk abin da ya fito yana sallah ba
zai cutar da shi ba, tun da in aka ce ya sake alwala yayin
fitowar kowacce tusa ba zai iya ba, zai kuma shiga cikin
wahala, Sharia ba ta dorawa rai sai abin da za ta iya, kamar
yadda ayoyi da hadisai da yawa suka tabbatar da haka. Babu
takurawa da kunci a cikin Addinin musulunci kamar yadda
ayar karshe a suratul Hajji ta tabbatar da hakan. Don neman
Karin bayani duba: Alfawakihuddawany na Annafraawy
1\340.
Amma idan tusar ba'a mafi yawan lokuta take fitowa ba ya
wajaba ya sake alwala duk sanda ta fito, saboda sallah ba ta
ingantuwa saida alwala. Kula da wasuwasin abu ne mai
muhimmancin gaske, saboda da yawa Shaidan yake busa a
duburar dan'adam amma ba tusa ba ce, wanda ya ji haka, to
kar ya fita daga sallarsa, har sai ya ji iska ko kara ta fita,
kamar yada hadisin Bukhari ya tabbatar da hakan.
Dr Jamilu Yusuf Zarewa
24/04/2016
94
bashi ya bari za ka biya masa? sai yace E,sai Annabi (s.a.w)
yace to ai bashin Allah shi ya fi cancanta a biya, don haka ka
yi masa hajj, kamar yadda Ibnu Taimiyya ya rawaito a
Muntaka hadisi mai lamba ta:1797, da kuma Darakudni.
Sannan Kathamiyya ta tambayi a Annabi (s.a.w) cewa: Hajji
ya riski babanta ya tsufa zata iyayi masa? sai Yace E, kamar
yadda Bukari ya rawaito a hadisi mai lamba ta;1756.
Malaman fiqhu sun kafa hujja da Wadannan hadisan
tabbatattu kan halacci ko wajabcin yiwa mamaci ko Wanda
bazai iya ba aikin hajji Idan yana da halı. Hajji ibada ce mai
zaman kanta,kuma daya daga cikin ginshikan musulunci
babu yadda za'a yi wata addu'a ta zauna a makwafinta.
Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa.
29\4\2016
96
shi, wanda ya bı son zuciyarsa, to Allah yana nan a
madakata.
Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa
05/05/2016.
97
iyakance lokacin da ake fara jima'i da mace ba. Don neman
karin bayani duba: AlMugni 27/77 da kuma Alminhaj na
Nawawy 9/206.
Allah ne mafi sani
Dr Jamilu Zarewa.
09\5\2016
98
ya saketa se mijin nata ya amince akan zai kawo mata
takardan sakin. Mallam a ranan da sukayi zai kawo mata
takardan sakin, kawai sae ta samu tsohon saurayinta akan ta
naso da zaran ta gama idda se ya aureta. Mallam menene
hukuncin wannan auren idon tagama idda ya aureta?
Na taba ji ance duk wanda ya nemi mace tana idda babu
aure a tsakanin su har abada, Mallam don Allah ka taimaka
mana da Karin bayani ?.
Amsa:
Wa alaikum assalam, in mutum ya nemi mace tana idda ya
aikata haramun, kamar yadda aya ta: (235) a suratul Bakara
ta tabbatar da hakan,saidai in an yi auran bayan ta gama
idda auran ya inganta, amma an aikata zunubin nema.
Malikiyya suna haramta mace ga mutum har abada in ya
aure ta cikin idda, ba in ya neme ta ba. Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa.
19/5/2016.
108. ZAN IYA AURAN 'YAR KANWAR MATATA?
Tambaya:
Assalamu alaikum Malam, Ya halatta mutum ya auri yar
qanwar matarsa?
Amsa:
Wa alaikum assalam, ya halatta ya aure ta, bayan ya saki
matarsa, amma bai halatta ya hada su ba saboda innarta ce,
Annabi s.a.w. yana cewa: "Ba'a a hada mace da goggonta,
ba'a hada mace da innarta a auratayya, saboda in kuka yi
haka, za ku lallata zumunci ku" kamar yadda ibnu Hibban ya
rawaito.Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Zarewa
99
20\5\2016
101
karamar yarinya bace tana da shekaru masu yawa, Don haka
ba tare da sun yi saduwa na aure oay a saketa. Bayan haka
tafiya ta oay aoi zuwa wani gari inda acan yasami yarinya
mai irin shekarun da yakeso sai sukayi aure. Bayan auren sai
ya zaman wacce ya auran ‘ yar wancan mata oay a sakane.
To anan Auren ya halatta ko kuma bai halatta ba a bisa ayoyi
ko kuma Hadisai na Annabi (S.A.W)?
Amsa:
Wa alaikum assalam, idan mutum ya auri mace sai ya sake
ta kafin su sadu, ya halatta ya auri ‘yarta kamar yadda aya
ta: 23 a suratun Nisa’I da kuma hadisin da Tirmizi ya rawaito
suka tabbatar da hakan. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Zarewa.
5/6/2016
102
kika gani zai zama ba jinin haila ba ne, tun da ya rasa daya
daga cikin siffofinsa. Allah ne mafi sani
Dr Jamilu Yusuf Zarewa
7 Ramadan, 1437H (12/06/2016).
103
ba zai kawo matsala tsakanin mu. Toh mallam yaya hukuncin
wannan abun?
AMSA: Wa alaikum assalam, ina ba ki shawara ki tambaye
shi, In har kin gano sihiri ne aka yi ya halatta ki ki dafawa, ko
da kuwa zai sake ki, saboda sihiri kafurci ne. Biyayya ga miji
dole ce kamar yadda hadisai da ayoyi suka tabbatar, saidai
babu biyayya ga abin halitta wajan sabawa mahalicci, kamar
yadda ayoyi a suratul Ankabuti da Lukman suka tabbatar da
hakan.
Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Yusuf Zarewa.
26 Ramadan, 1437H
105
10/7/2016
Tambaya:
Assalamu alaikum wa rahamatullahi wabarakaatuhu: Miji ne
ya je saduwa da matar sa sai ya kuskure ya saka mata a
dubura shin mene ne hukuncinsa?
Amsa:
107
Wa alaikumus salam wa rahamatullahi wa barakaatuhu, In
har da kuskure ya saka mata a dubura, sai ya yi maza ya
zare, mutukar ya cire daga zarar ya ji ba wurin ba ne Allah
ba zai kama shi da laifin hakan ba.
A karshen suratul Bakara "Ya ubangijinmu karka ka kamamu
in mun manta ko munyi kuskure" Muslim ya rawaito hadisi
cewa: Allah ya zartarda hakan. Ibnu-majah ya rawaito hadisi,
Annabi s.a.w. yana cewa: "Allah ya yafewa al'umata abin da
suka aikata cikin kuskure". Cigaba da jin dadi a wurin bayan
gano kuskuren, yana daga cikin zunubai. Allah ne mafi sani
Dr Jamilu Yusuf Zarewa
11 Shawwal, 1437 (16/07/2016).
Tambaya:
Amsa:
Dr Jamilu Zarewa
26/09 /2016
108
122. MEYASA AKA BAMBANTA NAMIJI DA MACE A
WAJAN RABON GADO?
Tambaya:
Assalamu alaikum mallam menene hukuncin wanda ke
kokarin ganin an baiwa mace kason da aka bawa namiji
wajen rabon gado?
Amsa:
Wa'alaikum assalam, Ya sabawa Allah, Hakan kuma zai iya
fitar da Shi daga musulunci in har ya yi gangancin haka,
saboda kokari ne na warware hukuncin da Allah ya zartar.
Allah da kansa ya raba gado bai wakilta wani don ya raba ba,
ya bawa kowa hakkinsa gwargwadon kusancinsa da mamaci
da kuma masalahar da Allah ya duba, wacce ya fi kowa
saninta.
Daga cikin hikimomin da suka sanya shariar Musulunci ta
bambanta tsakanin mace da namiji a rabon gado shi ne:
kasancewar hidimar namiji ta fi ta mace, yawanci mace idan
tana karama tana karkashin kulawar mahaifinta, idan kuma
ta yi aure tana komawa cikin kulawar mijinta.
Allah ya yi alkawarin wuta mai kuna ga duk Wanda ya
sabawa ayoyin rabon gado a cikin suratun Nisa'i aya:14,
kamar yadda ya yi alkawarin Aljanna mai koramu ga wanda
ya bi rabon da ya yi a cikin aya ta:13 a waccar Surat. Duk
Wanda ya kiyaye dokokin Allah tabbas zai kiyaye shi, Wanda
ya sabawa Allah, to yana nan a madakata, kuma mabuwayi
ne mai tsananin karfi kamar yadda ayoyin Alqur'ani masu
yawa suka tabbatar. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Zarewa
109
05/10/2016
110
iyayansa ma a wahalce, Saboda raunin jininsu Wanda yake
haddasa musu ciwon wasu daga cikin gabobinsu.
Zai yi kyau ma'aurata su yi gwaji kafin aure, in har dukkansu
suna dauke da kwayar Sikila (AS) su hakura da yin aure tare,
tun da za su haifi yaron da zai rayu a wahale, da rashin
Walwala gashi kuma addinin musulunci ya yi nufin sauki da
jin dadi ga al'uma. Dukkan wani abu ba ya faruwa sai da
kaddara, saidai riko da sababi abu ne da sharia ta tabbatar,
kuma ayoyi da yawa suka yi bayaninsa. Wanda yake (AS)
idan ya auri (AA) za su haifi 'ya'ya lafiyayyu da iznin Allah,
wannan sai ya nuna abin yana da yalwa.
Allah ne mafi Sani
Dr. Jamilu Zarewa
12/10/2016
NI.
Tambaya:
Assalamu alaykum, Malam ina da tambaya,mace ce bayan
mijinta ya sadu da ita, kafin ta yi wanka Sai jini ya xo mata
ya xa ta yi wanka, shin gabadai zatayi niyya ko kuma
wannan na biyun xa tayi?
Amsa:
Wa alaikum assalam, za ta jira in ta samu tsarkin haila sai ta
yi wanka daya kawai. Yana daga cikin ka'idojin SHARIA Idan
ibadoji guda biyu suka hadu, kuma manufarsu ta zama guda
daya, sannan za'a iya hada su a lokaci guda, to sai daya ta
shiga cikin dayar. Wannan yasa mai janabar da jinin haila ya
same ta kafin ta yi wanka, za ta wadatu da wankan karshe,
saboda saukin musulunci da kuma daukewa jama'a abin da
zai kuntata musu, kamar yadda aya ta karshe a suratul Hajj
ta tabbatar. Allah ne mafi Sani
Dr Jamilu Zarewa
11/09/2016
116
haramtawa, ita ce wacce yaro ya sha saboda yunwa” ,
Bukhari lamba ta : 5102, ma’ana lokacin da ba zai iya
wadatuwa ba daga nono, saboda shi ne abincinsa, shi kuma
wannan ya faru ne bayan mutum ya girma don haka ba zai yi
tasiri ba wajan haramta aure, wannan ita ce maganar mafi
yawan malamai.
2. Yana haramta aure, saboda ko da yaushe mutum ya sha
nonon mace to ta haramta a gare shi, domin Annabi s.a.w.
ya umarci matar Abu- huzaifa da ta shayar da Salim, don ta
haramta a gare shi, kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi
mai lamba ta : 2636, tare da cewa a lokacin Salim ya riga ya
girma, wannan sai yake nuna cewa idan babba ya sha nono
to zai yi tasiri wajan haramcin aure.
Zancen da ya fi karfi shi ne nonon da mutum ya sha bayan
ya girma ba ya haramta aure a tsakaninsa da matar da ta ba
shi.
Don neman Karin bayani duba : Bidayatul-mujtahid 2\67.
Duk wanda ya kiyaye dokokin Allah, tabbas zai kiyaye shi,
Wanda ya saba masa zai same shi a madakata.
Allah ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa
26/12/2016
NA AURA?
Tambaya: Assalamu alaikum, dafatan Malam yana cikin
qoshin lfy Allah sa haka amin. Malam inaneman shawara,
Wace mace yakamata na aura amatsayina na dan shekara
117
ashirin da takwas 28-29. yar shekara nawa tafi dacewa dani
a yanzu? Allah sa mudace amin .
Amsa:
Wa alaikum assalam, ka auri mai addini, wacce Idan ka
kalleta za ta burge ka, mai sonka, mai nutsuwa da sanin ya
kamata, yana da kyau ka Sami matar da ka fi ta kudi da ilimi,
ta fi sonka, ta kuma fika kananan shekaru, Ka tsaya ka
kalleta da kyau, kafın ka aure ta, kada ka yi gaggawa. Allah
ne mafi sani.
Dr Jamilu Zarewa.
16/03/2016
118
135. MAI HAILA ZA TA IYA TABA IZU GOMA?
Tambaya:Assalamu Alaikum, Malam. Wai gaskia ne mace
mai haila (period) zata iya rike Alqur'ani izu gima?
Amsa:
Wa alaikum assalam, Abin da yafi zama daidai Shi ne: kar
mai haila ta taba ko da wani bangare ne na Alqur’ani, saboda
hadisin Amru Bn Hazm, wanda wasu malaman hadisin suka
inganta, Inda Annabi S.a.w. Yake cewa: (Kar Wanda ya taba
Alqur'ani sai mai tsarki), kamar Albani a Sahihi wa dha'ifil
Jami'I hadisi mai lamba ta: 13738. Amma ya halatta ta
karanta ta hanyar kallo, saboda duk hadisan da suka hana
mai haila karatun Alqur'ani ba su inganta ba.
Allah ne mafi sani
Dr Jamilu Zarewa
4/01/2017
119
wani dan kitse da wani zare zare da yake fitowa:shin dan
Allah mallam ya zanyi na banbance jinin bari dana haila
kasancewar nayi bari akai akai harsau 5 haihuwa 1.
Amsa:
Wa'alaykumussalam, Duk jinin da kika gani a BARIN da kika
yi bayan ciki ya kai wata hudu, sunansa jinin haihuwa, in
kuma bai kai ba sunansa jinin bari wanda baya hana sallah.
Dr Jamilu Zarewa
21/01/2017
120
138. MIJINA YANA CHARTING DA TSOHUWAR BUDUWARSA,
BAYAN TA YI AURE
Tambaya:
Assalamu alaikum, Allah ya taimaki Dr, mijina ne suke chat
da wata matar aure, wadda tsohuwar budurwarsa ce a baya
sama da shekara 20 da wani abu ta yi aure, suna turawa
juna hotuna, shin malam wata shawara da nasiha ya kamata
na yi masa? Saboda kubutar da su ga fadawa halaka. Allah
ya taimaki mallam ya kara fahimta.
Amsa:
Wa alaikum assalam, Ki yi masa nasiha da tsoran Allah,
sannan kuma ki nuna masa cewa: Inda matarsa ce ba zai so
ayi irin wannan mua'malar da ita ba. Yin charting irin
wannan da matar aure yana iya kaiwa zuwa zina,
musamman da alama har yanzu suna son juna, Allah ya
hana duk abin da zai kusantar zuwa Zina a suratul Isra'a'i.
Zunubi shi ne abin da ya maka kaikayi kuma ka ji tsoran kar
mutane su yi tsinkayo akai.
Wanda ya kiyaye Allah zai kiyaye Shi, wanda ya saba masa
zai hadu da Shi a madakata. Dayanku ba zai yi cikakken
imani ba har sai ya sowa dan'uwansa abin da yake soma
kansa. Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
4/4/2017
121
Assalamu alaykum. Malam ya ibada? Allah ya samu dace.
Malam don Allah ina son nasan matsayin aurena shekara
daya mijina be kusanceni ba alhalin muna tare kuma
dukkanin mu muna lafiya. Nagode .
Amsa:
Wa alaikum assalam, Auranku ingantacce ne,, amma zai yi
kyau a kira magabatanku a tattauna matsalar, tun da
saduwar ma'aurata ginshiki ne na Zamantakewar aure,
wanda rashinsa yana kai ma'aurata zuwa saɓon Allah. In har
ba ku cimma matsaya ba, bayan zama da magabata kina iya
kai shi Kotu alkali ya muku hukunci, Saboda a musulunci bai
Halatta miji ya kauracewa matarsa ba sama da wata (4)
kamar yadda aya ta (226) a suratul
Bakara ta tabbatar da haka. Allah ne mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
08/06/2017
122
ba, kamar yadda aya ta (229)a suratul BAKARA ta tabbatar
da hakan.
À zance mafi inganci Kul'i yana saukar da saki daya, saidai
yana nisanta mace da mijinta ta yadda ba zai iya saké zama
da matar ba, sai in ya bayar da SADAKI sannan an kara
daura sabon aure.Allah ne mafi sani
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
20/06/2017
123
142. TA HAIHU KAFIN TA CIKA WATA BAKWAI DA
AURE?
Tambaya: Assalamu Alaikum. Malam yarinya ne aka aurar
da ita ba tayi
wata bakwai ba 7 ta haihu cikakkiyar yarinya yar wata tara
(9) to malam
meye hukuncin auren kuma ya hallaccin jaririyar a
musulunci?
Amsa: Wa'alaikum salam,In har an San tana da ciki aka yi
auran wannan hukuncinsa a fili yake, kuma auran bai
inganta ba a zance mafi inganci, amma in haihuwa ta yi
Kafin ta cika wata bakwai, kuma ba'a santa da ciki ba to
dansa ne, saboda ayar suratu Lukman da tá suratul Ahkafi
sun nuna cewa ana iya haife ciki a watanni shida.Auran dá
aka yi dá cikin shege ba tare da an sani ba ya inganta, saidai
ba zá'à danganta cikin zuwa mijin ba, tunda ba shi ya yi ba.
In har ya san tana da ciki bayan sun yi aure bai halatta ya
take ta ba har saí ta haihu, saboda fadin Annabi s.a.w. "Duk
wanda ya yi imani dá Allah da ranar Lahira to kar ya shayar
da ruwansa ga shukar waninsa" kamar yadda Abu-dawud ya
rawaito. In ta haihu za su iya cigaba dá mu'amalarsu ta aure,
musamman in bai sani ba saí dá aka daura.Allah ne mafi
sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
07/08/2017
124
Tambaya:
Assalamu alaikum malam, tambaya ce dani. Mijina ne
yasake ni sau biyu, sai yasha abin maye yace na zo
nasameshi, nii kuma banzoba saboda bana son abin da
yakesha na maye, shine yace idan banzoba a bakin aure na.
Shin yaya auren mu? Allah ya saka da alheri.
Amsa:
Wa alaikumus salam, Malamai sun yi sabani game da
aukuwar sakin wanda yake cikin maye: akwai maganganu
guda biyu:
1. Mafi yawan malamai sun tafi akan cewa idan ya saki
matarsa, tabbas sakin ya auku, saboda shan giya sabon
Allah né, kuma shi ya jawowa kansa, don haka ba za'à
yi masa uzuri ba, wannan ita ce maganar Abu-hanifa da
Malik da Shafii a daya daga cikin zantukansu.
2. Sakinsa bai auku ba, saboda lokacin dá Má'iz ya zo ya
tabbatarwa Annabi S. A. W. ya yi zina saidá ya tambaye
shi ko ka sha giya né, kamar yadda Baihaki ya rawaito a
Sunanul-kubrah, hakan saí ya nuna mashayin giya ba'a
amsar maganarsa. Sannan an rawaito daga sayyadina
Usman da Ibnu Abbas cewa : sakin mashayin giya ba ya
aukuwa, kuma ba'a san wanda ya Sabá musu ba a cikin
Sahabbai.wannan ita ce maganar Imamu Ahmad da
Zahiriyya da Ibnu Taimiyya.
Babban Muftin Saudiyya na waccan lokacin Sheik
Abdulaziz bn Bazz da wasu Malaman suna rinjayar da
magana ta biyu saboda mashayin giya bai san abin da
yake fada ba, hakan sai ya sa ya yi kama da Mahaukaci
125
wanda Alkalami ya saraya daga kan shi, kai har sallah
ma an hana mashayin giya ya yi saboda ba ya cikin
hayyacinsa, kamar yadda aya ta (43) a Suratu Annisa'í
ta tabbatar da hakan. Don neman karin bayani duba :
Al-Mugni 7/289 dá kuma Sharhul Munti'i 10/233.
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
9/08/2017
126
fadawa hadari ya wajaba a kula da su, mutukar bai sabawa
sharia ba, tun da musulamai suna kan sharudansu ne kamar
yadda hadisi ya tabbatar.
Allah ne mafi sani
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
28/08/2017
127
Wa alaikum assalam,To dan'uwa Layu da guru sun kasu
kashi biyu:
1. Layun da aka yi su da Sakandami ko Hatimi ko sunayan
aljanu ko wani abu na daban wanda ba Qur'ani ba,
wannnan malamai sun cimma daidaito game da
haramcinsu kamar yadda ya zo a Fataawaa Allajna
Adda'imah 1/212 saboda fadin Annabi S.A.W. (LAYU da
kuma abin da ake daurawa mace don miji ya sota shirka
ne) kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi mai
lamba ta: (3883) kuma Albani ya inganta shi, sannan da
hadisin da Imamu Ahmad ya rawaito mai lamba ta:
(16969), inda Annabi S.A.W. yake cewa: (Wanda ya rataya
laya to ya yi shirka), shima wannnan hadisin Albani ya
inganta shi a Silsila Sahiha. Hadisan da suka gabata suna
nuna haramcin daura Laya saboda Manzon tsira ya kira ta
da shirka, shirka kuma tana fitar da mutum daga
musulunci.
2. LAYUN da aka yi su daga Alqur'ani ko hadisai ingantattu,
wadannan na'u'i malamai sun yi sabani akansu:
A. Sun halatta saboda sun kunshi sunan Allah da kuma
karatun alqur'ani wanda sifar Allah ce, wanda ya dogara da
su ya dogara ga Allah, wannan ita ce maganar Amru bn Al-
ass da Aisha da wasu daga cikin magabata.
B. Ba su halatta ba saboda Ba'a samu Annabi S.A.W. ya yi
ba, da hakan sharia ne da an gan shi ya yi ko da sau daya ne
a rayuwarshi, sannan rataya layun da suke dauke da
Alqur'ani zai jawo a wulakanta su tun da za'a shiga wurare
128
marasa tsarki da su lokacin biyan bukata, kiyaye hakan
kuma yana da kamar wuya.
Zance mafi inganci shi ne haramcin amfani da Layun da suke
daga Alqur'ani saboda dukkan alkairi yana cikin biyayya ga
manzon Allah S.A.W, sannan shariar musulunci ta halatta
mana addu'o'i da yawa na neman kariya wadanda suka
wadatar da mu daga layu. Don neman karin bayani duba:
Taisirul Azizil Hamid shafi na : (136) da kuma Ma'arijul Kabul
2/510
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
4/10/2017
131
shine nake son a mika min wannan tambaya ga malaman
Allah yataimaka amen.
Amsa:
Wa alaikum assalam, To ɗan'uwa auran da kafurai suka yi
kafin su musulunta ingantacce ne mutukar sun yi shi akan
ƙa'idoji da sharuɗan da suka yarda da su na auratayyarsu,
saboda Annabi S. A. W bai canza auran kafiran da suka
musulunta ba a zamaninsa, ya tabbatar da su kuma ya yarda
da 'ya'yansu da suka haifa ta hanyar wancan aure.
Sahabban Annabi S. A. W. da yawa an haife su ne ta hanyar
auratayyar zamanin maguzanci kuma musulunci ya yarda da
dangantakarsu zuwa iyayansu, wannan ya sa duk ɗan da
kafurai suka haifa ta hanyar aure za mu danganta shi zuwa
iyayansa bayan sun musulunta. In kafirai suka yi zina suka
haifi Ɗa ba za'a danganta shi zuwa babansa ba bayan ya
musulunta. Don neman karin bayani duba:
Al-mugni na Ibnu Ƙudama 7/115 da kuma
sharhulMumti'i12/239.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
13-09-1438/ 08-06-2017
151. TA KI YARDA DA MIJINTA SABODA TANA AZUMIN NAFILA!
Tambaya: AssalamuAlaikum.Mallam ina da tambaya? Yaya
hukuncin Matar da miji ya bukacheta tana Azumin sunna. Taki
ta aminche mishi
Amsa: Wa alaikumus salam, ta yi kuskure ya kamata ta amsa
kiran mijinta, saboda azumin sunna ya halatta a karya shi ko
da babu dalili, Annabi (SAW) yana cewa"Mai azumin nafila
sarkin kansa ne ina ya Ga dama ya cigaba da azumin, in
132
kuma ya so ya karya " kamar yadda Tirmizi ya rawaito a
Sunan.
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
30/1/2018